RFI Hausa
@ha.rfi.fr
44 followers
6 following
3.2K posts
🌍 Sashen Hausa na RFI na maraba da ku a shafin Bluesky
💻 rfi.fr/ha/ 🎧 rfi.my/kai-tsaye
𝕏 rfi.my/Xha 📷 rfi.my/IGha 🗨️ rfi.my/WAha
Posts
Media
Videos
Starter Packs
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 5h
Dole mu samar da kariya ga sararin samaniyar Ukraine - Zelensky
Shugaba Volodymyr Zelensky, ya bukaci hukumomin tsaron ƙasar, da su kare sararin samaniyar Ukraine, sa'o'i bayan hare-haren bam na Rasha da suka kashe mutane huɗu tare da raunata wasu kimanin ashirin cikin dare.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 13h
An fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasar Ivory Coast
Al’ummar Ivory Coast sun fara kaɗa ƙuri'a domin zaɓen sabon shugaban da zai jagorancin ƙasar, tsakanin shugaba Alassane Ouatarra mai shekaru 83, wanda ke neman wa'adi na huɗu da kuma ƴan takarar jam'iyun adawa duk da cewa an hana jagororinsu tsayawa takara a zaɓen.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 14h
Mauritius ta kama Ravatomanga makusanci ga hamɓararren shugaban Madagascar
Hukumomi a Mauritius sun kama Mamy Ravatomanga, ɗaya daga cikin attajiran Madagascar kuma makusanci ga hambararren shugaban ƙasar da ake nema ruwa a jallo, bisa zargin miƙa wasu jiragen ƙasar ƙirar Boeing zuwa Iran.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 14h
Majalisar Ɗinkin Duniya ta daina aikin da aka samar da ita don shi - Lula da Silva
Shugaban Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya caccaki Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran cibiyoyi daban-daban, yana mai cewa sun daina aikinsu kuma sun gaza kare waɗanda yaƙin Gaza ya shafa.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Zelensky na taro da ƙawayensa yayin da Rasha ta ƙwace ƙarin garuruwa 4 na Ukraine
Shugaba Volodymyr Zelensky na ƙasar Ukraine, ya isa birnin London a yau Juma’a, domin tattaunawa da ƙasashen nan na ƙawance da suka yi alƙawarin tabbatar da zaman lafiya a ƙasarsa, da zarar an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Mamaye yammacin Kogin Jordan zai wargaza shirin zaman lafiyar Gaza- Amurka
Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya jaddada gargaɗin cewa mamaye yankin Yamma da Kogin Jordan na Falasɗinawa zai wargaza shirin shugaba Donald Trump na kawo ƙarshen yaƙin Isra’ila da Hamas.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Zulum ya nuna damuwa game da harin jirgi maras matuƙa da Boko Haram suka kai Borno
A Najeriya, gwamnan Borno Babagana Umara Zulum ya nuna damuwa game da harin jirgin maras matuƙa na bazata da mayaƙan Boko haram suka ƙaddamar a jihar, yana mai ganin baiken jami'an tsaron bayanan sirri wajen daƙile harin tun kafin a kai shi.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Shugaba Tinubu ya kori manyan hafsoshin tsaron Najeriya
Shugaban Najeriya ta kori manyan hafsoshin tsaron ƙasar da suka haɗa da Janar Christopher Musa, inda ya maye gurbinsa da Janar Olufemi Oluyede wanda zai ci gaba da riƙe muƙamin hafson hafsoshi. Wannan na zuwa ne bayan ƴan kwanaki ƙalilan da wasu jaridun ƙasar suka rawaito cewa, an yi yunƙurin juyin mulki a Najeriyar, amma shalkwatan tsaron ƙasar ta musanta.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Nijar: An dawo gudanar da zaman kotu a Diffa bayan shafe shekaru ana yi a Yamai
A Jamhuriyar Nijar, a karon farko an dawo gudanar da zaman kotu a Diffa, inda za’a saurari ƙararrakin mutane 65 da ake tuhuma da aikata laifukan daban-daban, da suka haɗa da ta’addanci, da safarar makamai tare da mallakarsu ba bisa ƙa’ida ba.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Benin ta haramtawa jagoran 'yan adawa tsayawa takara a zaɓen ƙasar
Hukumar zaɓen Jamhuriyyar Benin CENA, ta bayyana cewa ta cire sunan jagoran babbar jam’iyyar adawa ta Democrats Party daga jerin ‘yan takarar da zasu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da ke tafe a shekara mai zuwa.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 1d
Gobe Asabar al'ummar Ivory Coast za su ƙaɗa ƙuri'a a babban zaɓen ƙasar
Gobe Asabar ne ake sa ran gudanar da babban zaɓen shugaban ƙasa a Ivory Coast, a wani yanayi da ƴan takara 4 ke shirin ƙalubalantar shugaba mai ci Alassan Ouattara, ciki har da mai ɗakin tsohon shugaba Laurent Gbagbo wato Simone Gbagbo.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Hukumar PCC a Najeriya ta sanar da ƙarbar ƙorafe-ƙorafen jama'a fiye da miliyan 1
Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Jama'a ta Najeriya ta yi bikin cika shekaru 50 da kafuwarta, inda ta bayyana cewa cikin waɗannan shekaru ta yi nasarar magance ƙorafe-ƙorafe sama da miliyan 1 da dubu 200 na ƴan ƙasar, cikin sama da miliyan 1 da dubu 800 da aka shigar mata.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Tarayyar Turai da Amurka sun sanar da ƙaƙabawa Rasha sabbin takunkumai
A yau alhamis Ƙungiyar Tarayyar Turai ta sanar da sanya sabbin takunkumai a kan Rasha, saboda yaƙin da take yi da Ukraine, a dai-dai lokacin da Amurka ta sanar da wasu takunkumai da za su shafi ɓangaren makamashi na ƙasar.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Majalisar Isra'ila ta amince da ƙudirin ci gaba da mamayar yankunan Falasɗinawa
Majalisar Isra’ila ta amince da ƙudirin da ke neman faɗaɗa mamayar ƙasar a yankin yammacin gaɓar kogin Jordan, yunƙurin da ke da nufin ƙwace kaso mai yawa na yankunan Falasɗinawan, lamarin da ya saɓa da dokokin ƙasa da ƙasa, wanda kuma tuni Amurka ta bayyana shi a matsayin yunƙurin da ka iya wargaza yarjejeniyar zaman lafiyar da ke tsakanin ƙasar da Hamas da nufin kawo ƙarshen yaƙin Gaza.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Gwamnatin Mali ta sallami wasu manyan jami'an soji tare da maye gurbinsu da wasu
A Mali, shugaban mulkin sojin ƙasar Janar Assimi Goita ya sallami wasu daga cikin manyan jami’an tsaro har guda 3, tare da maye gurbinsu da wasu, a wani yanayi da suke ƙoƙarin yaƙar matsalar mayaƙa masu iƙirarin jihadi dake ci gaba da ta’azzara a ƙasar.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Fiye da rabin rikice-rikicen da duniya ke gani na faruwa ne a Afrika- Rahoto
Wasu alƙaluma da ƙungiyar agaji ta ICRC ta fitar sun nuna cewa kashi 40 na rikice-rikicen da duniya ke fuskanta na faruwa ne a Afrika nahiyar da ke ɗauke da mutane aƙalla biliyan 1 da miliyan 400.
rfi.my
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
· 2d
Ƴansanda sun kama Ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore a wata kotu da ke Abuja
Rahotanni na tabbatar da cewa ƴansanda sun kama Ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore a wata kotu da ke Abuja.Sowore ne dai ya jagoranci zanga-zangar neman a saki mai fafutukar kafa ƙasar Biafra Nnamdi Kanu a ranar Litinin, kuma an ga lokacin da yake gudu yayin zanga-zangar da rahotanni suka tabbatar da cewa an kama wasu daga cikin waɗanda suka fantsama tituna a wannan rana.
rfi.my